Hukumar Kula da Jin dadin Alhazai ta Jihar Kano ta ce za ta maidowa maniyyata 359 kuɗaɗen su na Aikin Hajjin bana da suka biya, wanda ya kai kimanin Naira Miliyan 48.
Waɗan nan maniyyata 359 ɗin sune waɗan da suka miƙa buƙatar a maido musu da kuɗaɗen nasu daga cikin maniyyata 1,794 da suka bada kuɗin ajiya.
Shugaban hukumar, Alhaji Muhammad Abba Ɗambatta ya ce waɗan da za a maidowa da haƙƙunan na su na daga ƙananan hukumomi 10 cikin ƙananan hukumomi 44 na jihar