Sarkin Zazzau ya rasu lokacin da ake buƙatar irin su- NAHCON

0
489

 

 

Daga Mustapha Adamu

 

Hukumar Hajji ta Ƙasa, NAHCON, ta bayyana cewa Marigayi Sarkin Zazzau, Alhaji Dakta Shehu Idris ya rasu ne a lokacin da ake matuƙar buƙatar irin su wajen cimma ƙudurin gwamnatocin tarayya da na Jihohi na kawo haɗin kai a Nijeriya.

 

A wata sanarwa da Jami’ar Hulɗa da Jama’a ta NAHCON, Fatima Sanda Usara ta fitar a ranar Litinin, Hukumar ta bayyana alhinin ta na rasuwar Mai Martaba Sarkin Zazzau ɗin.

 

Sanarwar tace a madadin Shugaban hukumar, Barista Zikrullah Kunle Hassan, a madadin manyan jami’ai da ma’aikatan ta, NAHCON na jimamin rasuwar Sarkin wanda yake mutum ne na mutane.

 

”NAHCON na miƙa ta’aziyar ta ga Shugaban Ƙasa , Muhammadu Buhari da Gwamna Nasir El-Rufai na Kaduna, iyalan mamacin da kuma ɗaukacin al’ummar Jihar Kaduna a bisa babban rashin da aka yi.

 

”Muna addu’ar Allah Yai masa rahma, Ya sa aljannar firdausi ce makomar sa. Allah Ya bawa iyalin sa juriyar rashin sa,” in ji sanarwar

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here