Hajjin bana: Ranar Alhamis za a fara jigilar alhazan Kano zuwa Nijeriya

0
355

Zuwa yanzu dai alhazan jihar sun cika da murna yayin da Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta jihar Kano ta bayyana gobe Alhamis a matsayin ranar da za’a fara aikin jgilar dawo da alhazan gida Najeriya.

Haka kuma a ranar 31 ga wata za’a akai alhazan jirgin karshe zuwa birnin Madina.

Babban Sakataren Hukumar Ambasada Muhammad Abba Danbatta ne ya bayar da tabbacin haka a garin Makkah a yau Laraba.

Ya ce dukkanin shirye-shirye sun kammala domin fara kwasar alhazan zuwa gida Nijeriya.