Hajjin 2023: Maniyyaciya da ga jihar Bauchi ta rasu

0
484
TOPSHOTSMuslim pilgrims perform the final walk (Tawaf al-Wadaa) around the Kaaba at the Grand Mosque in the Saudi holy city of Mecca on November 30, 2009. The annual Muslim hajj pilgrimage to Mecca wound up without the feared mass outbreak of swine flu, Saudi authorities said, reporting a total of five deaths and 73 proven cases. AFP PHOTO/MAHMUD HAMS (Photo credit should read MAHMUD HAMS/AFP/Getty Images)

Allah Ya yi wa maniyyaciya daga Jihar Yobe, Fanna Hassan, rasuwa a Sansanin Alhazai da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Jami’in alhazai na shiyya na Hukumar Aikin Hajji ta Najeriya (NAHCON), mai kula da shiyyar Maiduguri, Alhaji Wali Gana ne ya shaida wa HAJJ REPORTERS rasuwar marigayiyar da safiyar Asabar.

A cewar jami’in, marigayiyar na ɗaya daga cikin rukunin farko na maniyyatan Jihar Borno da aka tsara yin jigilarsu zuwa ƙasa mai tsarki.

Ya ƙara da cewa, “An shirya jirginsu zai tashi da misalin ƙarfe 11:00 na safe wanda shi ne rukunin farko na maniyyatan Jihar Yobe amma sai Allah Ya yi mata cikawa bayan sallar asuba a sansanin, ikon Allah ke nan.”

Da fatan Allah Maɗaukaki Ya gafarta kura-kuranta, kana Ya sanya ta a Aljanna Firdausi, amin.